Home BusinessKamfanin man fetur na Najeriya, NNPC, ya tabbatar da fashewar da ta faru a ranar Laraba a wasu al’ummomi biyu da ke kusa da masarautar Gbaramatu ta jihar Delta mai arziƙin mai.

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPC, ya tabbatar da fashewar da ta faru a ranar Laraba a wasu al’ummomi biyu da ke kusa da masarautar Gbaramatu ta jihar Delta mai arziƙin mai.

A wata sanarwa da kamfanin ya fitar a ranar Alhamis da yamma, ya ce har yanzu ba a gano musabbabin fashewar ba, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike.

NNPC ba ta bayyana adadin lalacewar da ta faru ko asarar rayuka.

Kamfanin ya ce an ƙaddamar da matakan gaggawa tare da haɗa kai da hukumomin tsaro da shugabannin al’umma domin ɗaukar matakan da suka dace.

“Abu mafi muhimmanci a wannan lokaci shi ne kare rayukan al’ummomin da ke kusa da wurin da kuma kiyaye muhalli,” in ji jami’in hulda da jama’a na NNPC, Andy Odeh.

NNPC ta bayyana cewa an gano raguwar ƙarfi a daya daga cikin manyan bututunta, wanda ke nuna yiwuwar fitar mai, lamarin da ya sa aka fara binciken farko.

Fashewar bututun mai ba sabon abu ba ne a Najeriya, inda kungiyoyin masu tayar da ƙayar baya ko masu satar mai ke yawan lalata bututun domin sace man fetur.

You may also like

Leave a Comment