Home NewsNEDC ta samar da jiragen ruwa na ceto, rigunan rai, abinci da tallafin NFI ga al’ummar Nguru Garbi, da sauran yankunan da ke gabar kogin Yobe

NEDC ta samar da jiragen ruwa na ceto, rigunan rai, abinci da tallafin NFI ga al’ummar Nguru Garbi, da sauran yankunan da ke gabar kogin Yobe

Hukumar Raya Yankin Arewa maso Gabas, **North East Development Commission (NEDC), ta kai dauki ga al’ummar Garbi da ke karamar hukumar Nguru a Jihar Yobe, tare da sauran yankunan da ke gabar kogin Yobe, inda ta samar da kayayyakin ceto da na jin kai. Tallafin ya zo ne bayan mummunan hatsarin kwale-kwale da ya faru a watan Janairun 2026, wanda ya yi sanadiyyar asarar rayukan fasinjoji da ke kan hanyarsu daga al’ummar Adiyani a karamar hukumar Guri ta Jihar Jigawa zuwa Garbi a karamar hukumar Nguru ta Jihar Yobe. Kayayyakin da aka bayar sun hada da rigunan kariya na ruwa (rigunan rai), jiragen ruwa masu sauri da na’urar hydraulic, jiragen ruwa masu faifan ruwa, famfo da sauran kayan aikin ceto. Haka kuma an raba kayan abinci da kayayyakin da ba na abinci ba, ciki har da tabarmi, barguna da kayan yara domin tallafawa iyalai da abin ya shafa da kuma wadanda suka fara kai dauki. Manajan Darakta na NEDC, Mohd G. Alkali, ya bayyana cewa hukumar ta kuduri aniyar ci gaba da bai wa gwamnatin Jihar Yobe goyon baya karkashin jagorancin Gwamna Mai Mala Buni, domin shawo kan matsalolin na gajeren lokaci da kuma samar da mafita ta dogon lokaci. Shi ma Kodinetan NEDC na Jihar Yobe, Farfesa Ali Ibrahim Abbas, ya yaba da hadin kan Sakataren Zartarwa na Hukumar Gaggawa ta Jihar Yobe, Dakta Mohammed Goje, da Shugaban Karamar Hukumar Nguru, Honarabul Muhammad Mairami, tare da sauran masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da cewa tallafin ya isa ga wadanda suka fi bukata. Daga Hussaini Tijjani Jallaba, Wakilin KANO LIVE 24, daga Jihar Yobe.

You may also like

Leave a Comment