93
Rahotanni sun ce jami’an ’yan sanda sun kama mutanen biyu ne bayan samun bayanan sirri game da shirin garkuwa da mutanen.
Binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargin sun shirya neman kuɗin fansa har Naira miliyan 22 bayan aiwatar da garkuwar.
A halin yanzu, ’yan sandan na ci gaba da gudanar da bincike domin gano sauran mutanen da ake zargin suna da hannu a shirin tare da gurfanar da su a gaban kotu.
Rundunar ta buƙaci jama’a su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai domin taimakawa wajen daƙile ayyukan masu laifi a jihar.