Home CrimeHedikwatar tsaro ta Nijeriya (DHQ) ta ba da umarnin gaggawa na cire dukkan shingayen bincike marasa izini a manyan hanyoyin ƙasar, bisa rahoton cewa suna rage ingancin aiki tare da jefa jami’an tsaro cikin haɗari.

Hedikwatar tsaro ta Nijeriya (DHQ) ta ba da umarnin gaggawa na cire dukkan shingayen bincike marasa izini a manyan hanyoyin ƙasar, bisa rahoton cewa suna rage ingancin aiki tare da jefa jami’an tsaro cikin haɗari.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa umarni ne wanda Birgediya Janar A. Rabiu ya sanyawa hannu a madadin Ministan Tsaro Christopher Musa, da ya bukaci kwamandoji su cire dukkan shingayen da ba su wajabta ba a yankunansu

Hanyoyin da abin ya shafa sun haɗa da Abuja–Lokoja–Enugu, Abuja–Kaduna–Kano, Abuja–Okene–Benin da Lagos–Ore–Asaba.

Ma’aikatar tsaron ta ce za a maye gurbin waɗannan shingaye da sintiri na musamman da kuma tattara bayanan sirri don inganta tsaro.

You may also like

Leave a Comment