Home NewsAn zargi Gwamnan Bauchi da biyan $9.7m don ɗaukar nauyin ta’addanci

An zargi Gwamnan Bauchi da biyan $9.7m don ɗaukar nauyin ta’addanci

A ranar Laraba, Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), ta gurfanar da Kwamishinan Kuɗi na Jihar Bauchi, Yakubu Adamu, tare da wasu mutum uku a gaban Kotun Tarayya da ke Abuja.

Ana zarginsu da haɗa baki wajen karkatar da kuɗin gwamnati da kuma amfani da kuɗin wajen ɗaukar nauyin ta’addanci.

Sauran waɗanda ake tuhuma sun haɗa da Balarabe Abdullahi Ilelah, Aminu Mohammed Bose da Kabiru Yahaya Mohammed.

Ana tuhumar su ne bisa dokokin hana safarar kuɗi da ɗaukar nauyin ta’addanci a Najeriya.

Mai shari’a Emeka Nwite, ya bayar da umarnin a tsare su a gidan gyaran hali na Kuje da ke Abuja.

Kotun ta ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 5 ga watan Janairu, 2026.

Dukkanin waɗanda ake tuhuma sun musanta laifin da ake zarginsu da shi.

You may also like

Leave a Comment