Home NewsGwamnatinmu bazatafadiba dukda tsananin zanga zanga,

Gwamnatinmu bazatafadiba dukda tsananin zanga zanga,

Gwamnatinmu bazatafadiba dukda tsananin zanga zanga,

 

Jagoran addinin Iran, Ayatolla Ali Khamenei, ya ce gwamnatin ƙasar ba za ta faɗi ba duk da tsananin zanga-zangar da ake yi a faɗin Iran, wadda aka bayyana a matsayin mafi muni cikin shekaru 15.

 

Khamenei ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a bainar jama’a karon farko tun bayan ɓarkewar zanga-zangar kusan mako biyu da suka gabata. A jawabin nasa, ya ce gwamnatinsa ba za ta lamunci mutane su riƙa aiki a matsayin sojojin hayar ƙasashen waje ko kuma masu yi wa ƙasashen waje aiki ba.

 

Dubban mutane ne ke ci gaba da gudanar da zanga-zanga a sassa daban-daban na ƙasar, inda suke kiraye-kirayen tumɓuke gwamnatin Iran, tare da zargin ta da gazawa wajen biyan buƙatun jama’a da kuma take haƙƙoƙinsu.

You may also like

Leave a Comment