Home NewsHukumar rubuta jarabawar shiga manyan makarantu ta kasa JAMB ta sanar da shirin tantancewa da amincewa da cibiyoyin jarabawar na’ura mai kwakwalwa guda 1,039 a faɗin Najeriya domin rubuta jarabawar shekarar 2026.

Hukumar rubuta jarabawar shiga manyan makarantu ta kasa JAMB ta sanar da shirin tantancewa da amincewa da cibiyoyin jarabawar na’ura mai kwakwalwa guda 1,039 a faɗin Najeriya domin rubuta jarabawar shekarar 2026.

Shugaban hukumar ta JAMB, Farfesa Is’haq Oloyede, ya bayyana hakan a Ilorin yayin zagayen tantance cibiyoyin.

Ya ce an tura masana 52 a jihohi daban-daban domin sake tantancewa cibiyoyin ko cire waɗanda ba su cika ƙa’idojin hukumar ba.

Ya ƙara da cewa aikin tantancewar yana tafiya yadda ya kamata, inda wasu cibiyoyi da aka taɓa samu da hannu a maguɗin jarabawa a baya suka sake bayyana, yayin da wasu suka sauya wurare domin ci gaba da aiki.

You may also like

Leave a Comment