109
Tajudden ya yi Alkawarinne ayayin
kaddamar da shirin kulawa da koshin lafiyar
masu Bukata ta musamman a Nigeria wada
ya gudana a Abuja.
Shugaban Majalisar Wakilan ta Nigeria
Tajudden Abbas wanda mataimakin
shugabqn kwamitin Makamashi na Majalisa
Joshua Gana ya wakilta ya ce a ko ina a
fadin duniya Kirkirarriyar fasaha ta na haifar
da sauyi a fannin kulawa da koshin lafiya.
Ya ce ta amfani da manhajar mai suna
(KOYO) majinyata a kasar nan za su iya cin
gajiyar samun kulawar gogaggun likitoci ta
hanyar amfani da shawarwarin kirkirarriyar
Fasaha a fannin kiwon lafiya daga bangarori
daban-daban.
Hakanan Shugaban majalisar wakilai ta kasa
ya yi Alkawarin samun goyon bayan
majalisar ta fuskar dokoki domin samun
dorewar shirin.