Home NewsƳanbindiga sun kai hari kan masana’antu a Mali

Ƴanbindiga sun kai hari kan masana’antu a Mali

Rahotanni daga Yammacin Mali na cewa mayaƙa masu iƙirarin jihadi sun kai hari kan wasu masana’antu da dama a tare da ƙona su.

An zargi iƙirarin jihadi mai alaƙa da al-Qaeda da hannu a lamarin, wanda ke nuna ƙarin yawan hare-hare kan manyan wuraren tattalin arziki a yankin.

Aƙalla mutum huɗu ne aka sace yayin hare-haren, kamar yadda rahotannin yankin suka bayyana.

An kai hare-haren ne kan masana’antu guda uku masu sarrafa siminti da sauran kayayakin gine-gine, ranar Lahadi a yankin Kayes.

Rahotanni daga yankin sun ce masu harin sun isa yankin a kan babura ɗauke da manyan makamai, kuma an ƙiyasta cewa sun kai tsakanin mutum 150 zuwa 200.

Yankin Kayes ya sha fama da irin waɗannan hare-hare a ‘yan watannin baya.

A watan Yuli, an zargi masu iƙirarin jihadi da kai hari kan masana’antu a wannan yanki, inda suka sace ma’aikata da dama, ciki har da wasu ‘yan Indiya.

You may also like

Leave a Comment