Home NewsKwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, ya buƙaci Rwanda da ta janye dakarunta daga gabashin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo, tare da tsawaita wa’adin aikin rundunar kiyaye zaman lafiya ta MDD a Congo da MONUSCO, na ƙarin shekara guda.

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, ya buƙaci Rwanda da ta janye dakarunta daga gabashin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo, tare da tsawaita wa’adin aikin rundunar kiyaye zaman lafiya ta MDD a Congo da MONUSCO, na ƙarin shekara guda.

A ƙudurin da aka amince da shi yayin zaman, kwamitin ya yi Allah wadai da farmakin da ƙungiyar M23 ke kaiwa tare da zargin samun goyon bayan Rwanda, yana kuma buƙatar Kigali ta daina tallafa wa ƴan tawayen ta kuma janye dukkan dakarunta.

Ƙudurin ya kuma tabbatar da ci gaba da aikin rundunar MONUSCO da ke da sojoji kusan 11,500 a faɗin ƙasar.

Wannan ƙuduri ya zo ne yayin da M23 ta ce ta janye daga birnin Uvira bayan matsin lamba daga Amurka, sai dai gwamnatin Congo ta ce janyewar wasan kwaikwayo ce kuma ƴan tawayen har yanzu suna cikin birnin.

You may also like

Leave a Comment