349
Tsawon shekaru ƙasashen duniya na kokarin gani an cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin sojojin Sudan da kuma rundunar sa kai ta RSF,wanda hakan ya ci tura.
Ƙungiyoyi a ciki da wajen ƙasar na bayyana cewa yaƙi ma na ƙara tsananta a yankin Kordofan da ke kudancin ƙasar, wanda hakan ya haifar da fargabar kisan gilla irin wanda aka yi a lokacin da RSF ta kama El-Fasher a ƙarshen watan Oktoba, inda rahotanni da dama suka ruwaito kisan gilla da fyaɗe da kuma kwacen kayan agaji.
Antonio Guterres ya bayyana a farkon wannan watan cewa ya na shirya tattaunawa da ɓangarorin biyu na ƙasar ta Sudan.