Home News‘Yansanda a Afirka ta Kudu sun ce ana shirin fara wani gagarumin aikin farautar wasu mutane bayan mutum tara sun mutu, wasu karin goma kuma sun ji rauni bayan da aka bude wuta a wani wurin shan barasa a yamma da birnin Johannesburg.

‘Yansanda a Afirka ta Kudu sun ce ana shirin fara wani gagarumin aikin farautar wasu mutane bayan mutum tara sun mutu, wasu karin goma kuma sun ji rauni bayan da aka bude wuta a wani wurin shan barasa a yamma da birnin Johannesburg.

Ƴansandan sun ce akwai kusan mutum 12 da ake zargi da harbin wadanda suka je wajen a wasu motoci biyu, suka kuma bude wuta.

A farkon watan nan ma akalla mutum 11, da suka hada da wani yaro aka harbe a wani haramtaccen wajen shan barasa a kusa da birnin Pretoria.

Afirka ta Kudu ta kasance daya daga cikin kasashen da aka fi kisan kai a duniya.

You may also like

Leave a Comment