Home NewsSheikh Isa Pantami Ya Yi Magana kan Rade Radin Cewa zai Auri Aisha Buhari  

Sheikh Isa Pantami Ya Yi Magana kan Rade Radin Cewa zai Auri Aisha Buhari  

Sheikh Isa Pantami Ya Yi Magana kan Rade Radin Cewa zai Auri Aisha Buhari

 

10 Jan 2026

 

Ibrahim Yusuf wanda ya yi bita Muhammad Malumfashi 3 – tsawon mintuna Sheikh Isa Ali Ibrahim Pantami ya fito karara ya musanta rade-radin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa yana shirin auren Aisha Buhari Tsohon minista, Pantami ya jaddada cewa marigayi Muhammadu Buhari uba ne a gare su, yayin da matarsa Aisha Buhari take a matsayin uwa Wasu jama’a sun yi martani karkashin sakonsa, suna bayyana cewa jita-jitar ba ta da tushe kuma gaskiya ta riga ta bayyana bayan ya yi bayani

 

Tsohon ministan sadarwa, Sheikh Isa Ali Ibrahim Pantami, ya yi karin haske kan rade-radin da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke alakanta shi da shirin auren uwargidan marigayi Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, Aisha Buhari. Pantami, wanda ya yi aiki a gwamnatin marigayi Buhari, ya bayyana rade-radin a matsayin kirkirarren labari mara tushe, yana mai cewa abin ya ba shi mamaki matuka.

 

Pantami ya wallafa sakon karyata shirin auren ne a Facebook bayan jita-jitar ta bazu sosai a kafafen sada zumunta, lamarin da ya haifar da muhawara da martani daga jama’a da dama a fadin kasa. –

You may also like

Leave a Comment