150
Jagoran juyin juya hali na Iran yayi Allah wadai da masu zanga zanga inda yace Amurka da Israel ne suke kuma kara rura watar.
Wannan na zuwa Kwana guda bayan da mahukuntan Iran suka katse layin Intarnet domin dakile yada hotuna a yayin da
zanga-zangar ta shiga kwana na 14 a jere.
A cewar kungiyoyi masu zaman kansu tuni zanga-zangar ta yi sanadiyyar mutuwar mutane da yawa inda su ka yi kira da a
mutunta hakkin dan Adam.
A ƙarshen watan Disamban shekarar 2025, aka fara zanga-
zangar bisa dalilai na matsin tattalin arziki kafin ta rikide zuwa
ta nema sauyin shugabanci.
Ko a ranar juma’a zanga-zangar nuna kin jinin gwamnati ta gudana a babban birnin kasar Teheran inda jama’a suka fita kan
muhimman hanyoyi.