90
Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bukaci dakarun sojin Nijeriya su cigaba da kasancewa masu ladabi, biyayya da haɗin kai, yana mai bayyana su a matsayin alamar ƙarfin bai ɗaya da kuma masu kare dimokuraɗiyyar ƙasa. Shugaban ya bayyana hakan ne ta bakin Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, a bikin Ranar Tunawa da Sojoji ta 2026 (AFCRD).
Tinubu ya ce walwalar sojoji ba ta rabu da tsaron ƙasa ba, inda ya ba su tabbacin ingantattun kayan aiki, horaswa da kyakkyawan yanayin rayuwa, tare da jaddada cewa gwamnatinsa za ta cigaba da tallafa musu domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin ƙasar.