Home CrimeWata kotu a Hong Kong ta gano wani babban dan jarida kuma mai rajin kare dimokradiyya, Jimmy Lai da laifin cin amanar kasa da kuma hada baki da wasu sojojin kasashen waje.

Wata kotu a Hong Kong ta gano wani babban dan jarida kuma mai rajin kare dimokradiyya, Jimmy Lai da laifin cin amanar kasa da kuma hada baki da wasu sojojin kasashen waje.

Mr Lai wanda ɗan asalin ƙasar Birtaniya ne, ya je kotun domin saurarar shari’ar.

Tuni dai Lai mai kimanin shekaru 78 da haihuwa ya soki hukuncin inda ya bayyana shi a matsayin bita da ƙullin siyasa.

Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗanadam da kuma ƙasashen yamma sun yi allawadai da hukuncin.

Lai shi ne fitaccen mutumin da aka fara tuhuma a ƙarƙashin wata dokar tsaron kasa mai cike da ce-ce-ku-ce wadda China ta ɓullo da ita a 2020.

You may also like

Leave a Comment