Home CrimeRunduar ’Yan Sandan Najeriya ta ce za a ci gaba da aiwatar da dokar izinin amfani da gilashi mota mai duhu da aka dakatar na ɗan lokaci.

Runduar ’Yan Sandan Najeriya ta ce za a ci gaba da aiwatar da dokar izinin amfani da gilashi mota mai duhu da aka dakatar na ɗan lokaci.

Shugaban Rundunar, Kayode Adeolu Egbetokun, ya sanar da haka tare da jaddada cewa babu wata kotu da ta hana aiwatar da tsarin, wanda za a fara ne daga ranar 2 ga Janairu, 2026.

Ya ce Hukumar ta yanke wannan shawara ne bayan ta lura da sabbin matsalolin tsaro da kuma buƙatar kare rayukan ’yan Najeriya.

Kakakin rundunar, Benjamin Hundeyin, ya ce an samu mummunan ƙaruwar laifuka ta hanyar amfani da motoci masu gilashi mai duhu ba tare da izini ba.

You may also like

Leave a Comment