Home NewsAn tsare tsohon ministan jamhuriyar Benin kan zargin juyin mulki

An tsare tsohon ministan jamhuriyar Benin kan zargin juyin mulki

Rahotanni daga Jamhuriyar Benin sun ce an tsare tsohon ministan tsaron ƙasar, Candide Azannai gabanin kammala shari’ar da ake ta zarginsa da hannu a yunƙurin juyin mulki a farkon watan nan.

Ofishin dillancin labaran Faransa ya ce ana zarginsa da yi wa ƙasa zagon ƙasa da kuma tunzura bore.

Mako ɗaya kenan da aka kama shi a hedikwatar jam’iyyarsa da ke kudancin birnin Cotonou.

Mr Azannai ya yi Allah wadai da yunƙurin kifar da gwamnatin shugaba Patrice Talon, inda aka kashe mutane da dama.

Tuni aka ɗaure mutane 30, mafi yawan su sojoji, inda ake zargin su da cin amanar ƙasa.

You may also like

Leave a Comment